Ana ci gaba da shari’ar tsohuwar ministar man fetur ta Nijeriya Diezani Alison-Madueke a kotun London, kan zargin ta da karbar cin hancin Yuro dubu 100
Gidan talabijin na Channels ya ruwaito cewa Diezani ta gurfana ne a gaban kotun Southwark Crown da ke Landan a kasar Birtaniya, domin fara sauraren shari’ar tuhumar da ake mata kan cin hanci.
Tun bayan kama tsohuwar ministar mai shekaru 65 a shekarar 2015 kafin bayar da belinta, ta musanta tuhume-tuhume shida da ake mata.
Za a fara cikakken zaman shari’ar ne a ranar 26 ga watan Janairun 2026.
