Masana harkokin lafiya sun bukaci Gwamnatin Tarayya da ta ba da fifiko wajen samarwa da wadatar da maganin harbin maciji (antivenom) a asibitoci fadin Nijeriya, yayin da rahotanni ke nuna cewa kasar na samun kusan harbin maciji 43,000 a duk shekara.
Manyan kwararrun lafiyar sun bayyana cewa karancin samun wannan muhimmin magani na ci gaba da haddasa mutuwar mutane da dama da maciji ke harba a kasar, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.
Sun kuma nuna cewa baya ga karancin maganin, wadanda harbin maciji ya shafa na kashe tsakanin N180,000 zuwa N250,000 a kan kashi daya na maganin, adadin da ya kai kusan albashin watanni hudu ga ma’aikacin da ke karbar mafi karancin albashi na N70,000 a Nijeriya.
A cikin wata sanarwar bayan wani taro kan kula da harbin maciji da hanyoyin bincike, wanda aka wata kungiya ta gudanar a Jami’ar Gombe, kungiyar ta bayyana lamarin a matsayin matsalar da aka yi watsi da ita, duk da irin barnar da take haifarwa a fadin kasar.
Ana samun harbin maciji kusan 43,000 a Nijeriya duk shekara – Masana
Recent Comments
on Gwamnatin Tinubu za ta fara ba da rancen maras kuɗin ruwa ga manoma da masu ƙananan sana’o’i – GEEP
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Jaridar Daily Trust ta gano dalilai uku da suka sa Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC na kasa
on Peter Obi ya sake jaddada bukatar kafa tsarin wa’adin shekara 5 kacal ga shugaban ƙasa a Najeriya
on Cire tsoffin ‘yan sanda daga daga tsarin Contributory Pension Scheme ya fi karfina – IGP Egbetokun
on Gwamnatin Nijeriya ta ɗage buɗe shafin neman aiki na Immigration, Civil Defence da sauran hukumomi
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An karkatar da Naira Bilyan 71.2 daga cikin Bilyan 100 na bashin dalibai a Nijeriya – Hukumar ICPC
on Gwamna Abba Gida Gida ya zabi tsohon shugaban ma’aikatansa da wasu mutum 5 a matsayin kwamishinoni
on Nijeriya za ta zama jagorar kasuwar halal ta duniya mai jarin Dala bilyan Dubu 7 – Kashim Shettima
