DCL Hausa Radio
f DCL HAUSA FACEBOOK
Saturday, April 11, 2026
HomeLabaraiAna son kansiloli su ƙaurace wa cin hanci a jihar Katsina

Ana son kansiloli su ƙaurace wa cin hanci a jihar Katsina

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya gargadi kansiloli 361 na mazabu a fadin jihar da su tsaya a kan gaskiya, bin doka da kuma riƙon amana wajen kula da muradun jama’a a matakin ƙasa.

Gwamnan ya yi wannan kira ne a wajen taron wayar da kai na musamman ga kansiloli a kan yaƙi da cin hanci, bin ƙa’ida da kuma tabbatar da gaskiya wajen aiwatar da manufofin gwamnati, wanda aka gudanar a Katsina.

Ya ce cin hanci na daya daga cikin manyan matsalolin da ke kawo cikas ga ci gaban ƙasa, yana ɓata albarkatu, yana rage amincewar jama’a da gwamnati, tare da lalata ingancin ayyukan raya ƙasa.

Radda ya bayyana cewa gwamnatinsa ta ƙarfafa Hukumar Karɓar Ƙorafe-ƙorafe da Yaƙi da Cin Hanci ta Katsina (KTPCACC) domin ta zama mai zaman kanta wajen kare gaskiya, adalci da gaskiya a gudanar da harkokin mulki.

Ya kuma jaddada cewa kansiloli su ne wakilan da suka fi kusa da jama’a, don haka dole ne su tabbatar da cewa duk wani aikin al’umma an aiwatar da shi yadda ya kamata, an kula da albarkatu yadda ya dace, tare da hana cin hanci da rashawa samun gurbi a matakin ƙananan hukumomi.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata