Tsohon gwamnan Abia, Sanata Orji Uzor Kalu, ya yi zargin cewa lallai an shirya yunkurin tsige shugaban majalisar dattawan Nijeriya Godswill Akpabio.
Da yake zantawa da manema labarai a majalisar, Kalu ya ce batun ba jita-jita ba ne, domin wasu ‘yan majalisa sun taba tattaunawa kan hakan, sai dai shirin bai yi nasara ba.
Kalu ya bayyana cewa shi da wasu abokan aikinsa ba za su taɓa yarda da irin wannan yunƙuri ba, yana mai kira ga ‘yan majalisa su fifita zaman lafiya, hadin kai da muradun kasa.
A kan batun tsaro, Kalu ya ce yana goyon bayan kalaman tsohon shugaban Amurka Donald Trump, yana mai bayyana cewa taimakon sirri da diflomasiyya daga Amurka na kara karfafa Nijeriya wajen yaki da ta’addanci.
