Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiAPC ta maye gurbin Uzodimma da Masari a shugabancin kwamitin taron ƙasa

APC ta maye gurbin Uzodimma da Masari a shugabancin kwamitin taron ƙasa

Jam’iyyar APC ta sauya Gwamnan jihar Imo, Hope Uzodimma, daga shugabancin kwamitin shirya babban taronta na kasa, inda ta naɗa tsohon Gwamnan Katsina, Aminu Bello Masari, a matsayin sabon shugaban kwamitin.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Sakataren Jam’iyyar APC na kasa, Surajudeen Basiru, ya fitar a ranar Jumma’a, gabanin taron ƙasa da APC za ta gudanar a ranakun 27 da 28 ga Maris, 2026.

Jaridar Punch ta rawaito cewa bayan shawarwari da jagorancin jam’iyya da manyan masu ruwa da tsaki, an sake fasalta kwamitin, inda aka sauya Hope Uzodimma ke takawa zuwa ma’aji treasurer.

Haka kuma jam’iyyar ta ƙara yawan mambobin kwamitin daga 73 zuwa 90, tare da shigar da sababbin jiga-jigan jam’iyyar.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata