Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya bayyana cewa jam’iyyar za ta yi nasara da rinjayen kuri’u a zaben 2027, yana danganta hakan da karɓuwar gwamnatin Shugaba Bola Tinubu.
Ya yi wannan bayani ne a Abuja yayin da yake karɓar kungiyar Women Leaders Support Advancement, inda ya ce Renewed Hope Agenda na Tinubu ya kara bude damar siyasa ga matasa da mata.
Jaridar Punch ta ambato Yilwatda ya bukaci mata su ci gaba da mara wa gwamnati baya, yana cewa su ne ginshikin karfin jam’iyya a ƙasa, musamman yayin da APC ke shirin taron Caucus na kasa da kwamatin zartaswa da aka dage zuwa 18–19 ga Disamba a Villa.
