Sunday, April 5, 2026
HomeSiyasaAtiku ya ce ɗansa na da 'yancin shiga APC kuma ra'ayinsa ne...

Atiku ya ce ɗansa na da ‘yancin shiga APC kuma ra’ayinsa ne na kashin kansa

Tsohon mataimakin shugaban Nijeriya, Atiku Abubakar, ya ce matakin ɗansa Abba Abubakar na shiga jam’iyyar APC zabin kansa ne, kuma bai da wani tasiri a kan siyasar sa ko tsayuwarsa kan matsalolin da suka addabi ƙasa.

Atiku ya bayyana cewa a dimokuraɗiyya, ’ya’ya na da ’yancin ra’ayi, kuma shi a matsayinsa na dattijo mai bin ka’ida, ba ya tilasta wa ’ya’yansa abin da ya saba musu — balle ma tilasta wa ’yan Nijeriya.

Sai dai ya jaddada cewa babban abin da yake damunsa ba batun sauyin jam’iyya ba ne, ƙuncin rayuwa da koma-bayan tattalin arziki da mulkin APC ya haifar wa ƙasa da talakawa.

A cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Atiku ya ce yana nan tsayin daka tare da sauran ’yan kishin ƙasa domin nemo mafita, dawo da ingantaccen mulki, da kawo sabuwar fata ga ’yan Nijeriya.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata