Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiAtiku ya zargi ICPC da son zuciya kan yunkurin kama El-Rufa’i

Atiku ya zargi ICPC da son zuciya kan yunkurin kama El-Rufa’i

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya zargi Hukumar ICPC da nuna son zuciya bayan abin da ya kira yunƙurin kama tsohon gwamnan Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai, a filin jirgin sama bayan dawowarsa ƙasa.

Atiku ya bayyana a shafinsa na X cewa ya kai wa El-Rufai ziyarar goyon baya, yana mai cewa an yi yunƙurin kama shi ba tare da gabatar da sammaci ba. Ya wallafa hotunan ganawar sirri da suka yi a wani gida mai zaman kansa.

Rahotanni sun ce jami’an tsaro sun yi ƙoƙarin tsaida El-Rufai a filin jirgin, amma daga bisani aka bar shi ya wuce bayan takaddama da ta ɓarke. Sai dai ICPC da sauran hukumomin tsaro ba su fitar da wata sanarwa a hukumance kan lamarin ba.

Lamarin na zuwa ne a daidai lokacin da ake samun zazzafar muhawara ta siyasa, bayan El-Rufai ya ƙara kusanci da jam’iyyar ADC tare da sukar gwamnatin tarayya a bainar jama’a kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata