Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiBa a take hakkin Kiristoci a Nijeriya ba - Babban hafsan tsaron...

Ba a take hakkin Kiristoci a Nijeriya ba – Babban hafsan tsaron Nijeriya

Babban hafsan tsaron Nijeriya Janar Olufemi Oluyede ya karyata ikirarin cewa ana zaluntar Kiristoci a Nijeriya, inda ya ce babbar matsalar Nijeriya ita ce ta’addanci.

Janar Oluyede ya bayyana hakan ne yayin zantawa da manema labarai a Abuja a ranar Litinin lokacin da ya mayar da martani kan kalaman shugaban Amurka Donald Trump wanda ya zargim ‘yan ta’adda na kai hare-hare kan Kiristoci.

Oluyede ya ce sojojin Nijeriya na aiki tuƙuru wajen yaƙar ta’addanci da tabbatar da tsaro, tare da samun nasara sakamakon sabon tsarin tsaro da shugaba Tinubu ya kafa.

Hakazalika ya ƙara da cewa rundunar soji za ta cigaba da ƙoƙari wajen dawo da zaman lafiya tare da buƙatar haɗin kan ƙasashen duniya domin yaƙi da ta’addanci.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata