Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiBa mu damu da batun tsige gwamnan Rivers ba saboda lamarin yana...

Ba mu damu da batun tsige gwamnan Rivers ba saboda lamarin yana gaban kotu – Gwamna Abdullahi Sule

Gwamnan Jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya ce gwamnonin jam’iyyar APC ba su cikin fargaba kan yunkurin tsige Gwamnan Jihar Rivers, Siminalayi Fubara, inda ya jaddada cewa batun yana gaban kotu kuma doka ce ke tafiyar da shi.

Gwamna Sule ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis yayin hirarsa a shirin Politics Today na tashar Channels Television, inda ya ce ba za a iya tsige gwamna kawai ba tare da bin tanadin doka da ka’ida ba, yana mai cewa gwamnonin APC na sa ido kan lamarin amma ba su ga dalilin firgici ba.

A halin yanzu dai, yunkurin tsige Gwamna Fubara ya tsaya cik bayan Babbar Kotun Jihar Rivers da ke Oyigbo ta dage sauraron shari’ar har sai Kotun Daukaka Kara ta yanke hukunci, yayin da Alkalin Alkalan jihar, Mai shari’a Simeon Amadi, ya ƙi kafa kwamitin bincike bisa umarnin kotu.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata