Ministan yada labarai da wayar da kai na Najeriya Alhaji Muhammad Idris ya bayyana cewa gwamnatin tarayya ba za ta yi bushasha a bikin cika shekaru 65 da samun ‘yancin kai ba.
Ministan ya yi wannan jawabi ne a wani taron manema labarai a Abuja, gabanin taron bikin tunawa da ranar ‘yancin kai, wanda za a gudanar a ranar 1 ga watan Oktoba mai kamawa, kamar yadda Daily Nigerian ta ruwaito.
Idris ya ce za a gabatar da wasu al’amura da suka hadar da addu’o’i bayan sallar Juma’a da kuma bayan gabatar da ibada ranar Lahadi, sai kuma muhawara tsakanin dalibai.
