Babban Hafsan Sojin ƙasa, Lt.-Janar. Waidi Shaibu, ya tabbatar cewa sojojin Nijeriya za su cigaba da aiwatar da ayyuka na karfi da akasin haka domin inganta tsaro a fadin ƙasar.
Shaibu ya bayyana haka ne yayin ƙaddamar da wata makarantar sakandare ta gwamnati mai azuzuwa 36 ta ‘Yan Mata da aka inganta a Maradun, Zamfara, a karkashin shirin na Musamman na Hadin Gwiwar Soji da Al’umma (Special Intervention Civil-Military Cooperation) na Maj.-Gen. Mamman Galadima.
A cewarsa, dangantaka tsakanin al’umma da sojoji dole ta kasance ta haɗin gwiwa domin mutane suna bukatar soji, kuma soji ba zai iya cimma burinsa ba ba tare da goyon bayan al’umma ba. Shaibu ya yi kira ga ‘yan ƙasa su cigaba da amincewa da sojoji tare da ba da goyon baya ga ƙoƙarinsu.
Har ila yau, Shaibu ya bayyana cewa irin waɗannan ayyuka na musamman suna nuni da yabo ga al’ummomin manyan hafsoshin soja, da kuma tallafawa jihohi wajen samar da muhimman ababen more rayuwa domin inganta rayuwar al’ummomin da ake amfana da su.
