Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiBabban lauya a Nijeriya Femi Falana ya soki Majalisar Dattawa kan yin...

Babban lauya a Nijeriya Femi Falana ya soki Majalisar Dattawa kan yin jinkiri wajen gyaran dokar zabe

Babban Lauya Lauya a Nijeriya Femi Falana, ya yi kakkausar suka ga Majalisar Dattawan Nijeriya kan jinkirta gyaran dokar zaɓe, yana mai gargaɗin cewa hakan na iya lalata sahihancin zaɓukan shekarar 2027.

Falana ya bayyana hakan ne yayin wata hira da ya yi a gidan talabijin na Arise a ranar Lahadi, inda ya nuna damuwa kan matakin majalisar dattawa na sake kafa wani kwamiti domin nazarin kudirin dokar, duk da cewa majalisar wakilai ta amince da shi tun watan Disambar 2025.

Ya ce wannan mataki ba wai anyi ne don gyara tsarin zaɓe ba, illa dai ƙoƙarin ci gaba da amfani da tsohon tsari da ke da kura kurai, yana mai cewa ana yaudarar ‘yan Nijeriya ne da suna cewa ana aiki kan dokar.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata