Monday, April 6, 2026
HomeKetareBabbar kotun kolin Guinée Conakry ta fitar da sunayen 'yan takarar da...

Babbar kotun kolin Guinée Conakry ta fitar da sunayen ‘yan takarar da ta amince da su

Babbar kotun kolin Guinée Conakry ta fitar da sunayen ‘yan takarar da ta amince da takardunsu ne a zaben shugaban kasar a ranar Asabar 8 ga watan Nuwamba 2025.

‘Yan takara 9 ne ta amince da takardun bukatar tasu ciki har da shugaban gwamnatin mulkin sojin kasar, Mamadi Doumbouya da ke kan karagar mulki tun 2021, bayan ya yi wa Alpha Condé juyin mulki.

Sai dai kotun ta yi watsi da wadansu takardun ‘yan takarar a kalla talatin.

A ranar 28 ga watan Disamba mai 2025, ne za a gudanar da zaben shugaban kasa a Guinée Conakry.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata