Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiBabu wata alama da ke nuna cewa Nijeriya za ta rushe -...

Babu wata alama da ke nuna cewa Nijeriya za ta rushe – Tukur Buratai

Tsohon babban hafsan sojin kasan Nijeriya, Laftanar Janar Tukur Buratai (rtd), ya ce maganganun da ke cewa Nijeriya na dab da rushewa ba su da tushe.

A wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Facebook, ya bayyana hakan a matsayin kalaman da ba su dace ba kuma ba su yi la’akari da tarihin dorewar kasar ba.

Buratai ya ce Nijeriya ta sha tsira daga rikice-rikicen siyasa, matsin tattalin arziki da kalubalen tsaro da ka iya karya wasu kasashe.

A cewarsa, sabon salo na shugabanci mai kishin kasa na fitowa a gwamnati da bangarori daban-daban.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata