Mai magana da yawun tsohon shugaban kasa Muhammad Buhari, Garba Shehu, ya karyata jita-jitar da ke yawo cewa akwai sabani tsakanin tsohon shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari da shugaba Bola Ahmed Tinubu.
A wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin na Trust TV a ranar Litinin, Garba Shehu ya bayyana cewa babu wata takaddama a hukumance tsakanin shugabannin biyu, yana mai cewa dukkansu har yanzu suna karkashin inuwa daya ta jam’iyyar APC.
Garba Shehu ya jaddada cewa tsohon shugaban kasa Buhari na ci gaba da biyayya ga jam’iyyar APC wadda ta ba shi damar zama shugaban kasa bayan kasa sau biyu a baya.
