Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiBangaren Peter Obi sun yi watsi da taron sulhun Datti Baba-Ahmed da...

Bangaren Peter Obi sun yi watsi da taron sulhun Datti Baba-Ahmed da Julius Abure suka jagoranta

Tawagar tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party a zaɓen 2023, Peter Obi, sun nesanta kansu daga wani taron sulhu da aka gudanar a ranar Litinin tsakanin mataimakinsa a takarar, Datti Baba-Ahmed, da shugaban jam’iyyar na ƙasa, Julius Abure.

A cikin wata sanarwa da magoya bayan Obi suka fitar, sun ce ba su da wani hannu ko wakilci a cikin zaman sulhun, wanda ke da nasaba da rikicin shugabanci da ke ci gaba da ƙara tsananta a cikin jam’iyyar.

Labour Party dai na fuskantar rikicin cikin gida, wanda ya ƙara tsananta tun watan Afrilu, bayan wasu mambobi uku na jam’iyyar sun yi iƙirarin cewa su ne shugabanni sahihai na jam’iyyar. Rikicin ya kai ga kotu, inda aka samu sabani kan sahihancin matsayin Julius Abure a matsayin shugaban jam’iyyar.

Sai dai duk da wannan sabani, hukumar zaɓe ta ƙasa, INEC, na ci gaba da amincewa da Julius Abure a matsayin shugaban jam’iyyar a hukumance, kamar yadda rahoton jaridar The Punch ya bayyana.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata