Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiBankin CBN ya yi gargadin hukunta masu wulakanta Naira

Bankin CBN ya yi gargadin hukunta masu wulakanta Naira

Babban Bankin Nijeriya, CBN, ya ƙara tsaurara matakan da yake ɗauka kan masu wulakanta takardar kuɗin Naira, inda ya yi gargaɗi ga ‘yan ƙasa da su daina liƙin kuɗi a wuraren bukukuwa, lalata su, yin jabun kuɗi ko kuma safararsu ba bisa ka’ida ba.

Bankin ya bayyana hakan ne a wajen Baje Kolin Kasuwanci na Ƙasa da Ƙasa na Kaduna, inda ya kuma yi bayani kan muhimman nasarorin da aka samu a ƙarƙashin shirye-shiryen gyaran da yake aiwatarwa.

Mataimakiyar Darakta a Sashen Hulɗa da Jama’a da Zuba Jari ta CBN, Mrs. Sidi Ali Hakama, ta ce girmama Naira wajibi ne a doka da ta ƙasa, tana mai bayyana kuɗin a matsayin alamar martabar Nijeriya.

Ta samu wakilci daga Mataimakin Darakta a Hedikwatar CBN da ke Abuja, Abbas Ibrahim Ahmed.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata