Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiBankin raya Afrika ya amince da bashin dala miliyan 46 domin gyaran...

Bankin raya Afrika ya amince da bashin dala miliyan 46 domin gyaran cibiyoyin lafiya a jihar Sokoto

Bankin Raya Kasashen Afirka ya amince da bayar da bashi na dala miliyan 46 domin tallafa wa shirin gyaran cibiyoyin lafiya a jihar Sokoto.

A cewar wata sanarwa daga bankin da jaridar Punch ta samu a ranar Juma’a, hukumar gudanarwar bankin ta amince da bashin ne domin magance matsalolin da suka dade suna hana samun ingantaccen kulawar lafiya a yankin.

Bankin ya bayyana cewa tsarin lafiya na jihar na fuskantar gagarumin kalubale, inda alamomi da dama ke nuna gazawa wajen inganci da isar da ayyukan lafiya ga al’umma.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata