Monday, April 6, 2026
HomeSiyasaBarnar da jam'iyyar APC ta yi wa Nijeriya ta zarta ta mulkin...

Barnar da jam’iyyar APC ta yi wa Nijeriya ta zarta ta mulkin soja – Atiku Abubakar

Tsohon mataimakin shugaban Nijeriya Atiku Abubakar ya zargi gwamnatin APC mai mulki da lalata tsari da yanayin kasar, yana mai bayyana ta a matsayin jam’iyya mai mulki mafi muni da ya taba gani.

Atiku ya bayyana hakan ne a Abuja yayin kaddamar da littafin sakataren jam’iyyar hadaka ta ADC Bolaji Abdullahi mai taken ‘The Loyalist’, inda ya ce ko a zamanin mulkin soji ba a samu barna irin ta APC ba.

A cewar sa, ya ji dadin haduwar ‘yan siyasa da dama wuri guda a cikin jam’iyyarsu ta ADC, a yunkurin sabunta fatan Nijeriya kan turbar dimukradiyya, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata