Sunday, April 5, 2026
HomeKetareBirtaniya na shirin ba matasa ‘yan shekaru 16 da 17 damar kada...

Birtaniya na shirin ba matasa ‘yan shekaru 16 da 17 damar kada kuri’a lokacin zaɓe

Gwamnatin Birtaniya ta sanar a ranar Alhamis cewa tana shirin sauya dokar zaɓe domin ba wa matasa masu shekaru 16 da 17 damar kada kuri’a a zaɓukan gama gari.

Matakin na zuwa ne bayan jam’iyyar Labour mai mulki ta sha alwashin aiwatar da sauyin tun kafin ta karɓi mulki a bara, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Haka kuma, yana ɗaya daga cikin jerin sauye-sauyen tsarin dimokuraɗiyya da gwamnati ke shirin aiwatarwa, musamman ganin yadda ƙasa ke fuskantar koma baya a sha’anin fitowar jama’a wajen yin zaɓe.

Sai dai ana sa ran matakin zai haifar da ce-ce-ku-ce, kasancewar masu adawa da sauyin sun taɓa zargin cewa yana da wata manufa ta siyasa, domin ana ganin matasa sun fi karkata ga jam’iyyar Labour mai ra’ayin hagu.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata