Jam’iyyar adawa ta ADC ta bayyana matsayarta kan nadin Farfesa Joash Amupitan a matsayin sabon shugaban hukumar zabe ta Nijeriya INEC wanda Shugaba Bola Tinubu ya gabatar.
A wata sanarwa da mai magana da yawun jam’iyyar, Bolaji Abdullahi ya fitar a ranar Alhamis bayan bayyana Joash a matsayin sabon shugaban hukumar, ya ce za su ba sabon shugaban hukumar damar nuna kwarewarsa wajen gyara tsarin zabe.
Jam’iyyar ta ce tana sa ran Farfesa Amupitan, wanda masani ne a fannin shari’a, zai dawo da martabar hukumar da kuma yarda tsakanin ‘yan kasa da idon duniya wajen gudanar da sahihan zabubbuka a Nijeriya.
Haka kuma ya kara da cewa, ya kamata sabon shugaban INEC ya san cewa biyayyarsa tana ga al’ummar Nijeriya, ba gwamnati ba kamar yadda Channels TV ta wallafa.
