Tuesday, April 7, 2026
HomeKetareBurkina Faso ta saki sojojin Nijeriya 11 da take tsare da su

Burkina Faso ta saki sojojin Nijeriya 11 da take tsare da su

Gwamnatin Mulkin Soji a Burkina Faso ta saki sojojin Najeriya 11 da ta tsare bayan jirgin da ya tashi daga Legas ya yi saukar gaggawa a Bobo-Dioulasso saboda matsalar na’urori.

Kungiyar kasashen kawance ta AES ta bayyana lamarin a matsayin “Rashin dattako,” inda jirgin na Nijeriya kirar C-130 ya shiga sararin samaniyar Burkina Faso ba tare da izininsu ba.

An tabbatar da cewa dakarun da ke cikin jirgin sun samu damar komawa Najeriya, duk da har yanzu ba a bayyana ko an saki jirgin ba.

Gidan Talabijin na TVC ya ruwaito jirgin ya sauka ne bisa ka’idojin tsaro na kasa da kasa yayin tafiya zuwa Portugal.

Kakakin Rundunar Sojin Sama ta Najeriya, Ehimen Ejodame, ya ce an yi bincike, kuma sojojin da aka tsare an kula da su yadda ya kamata, yayin da ake shirin ci gaba da aikin jirgin.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata