Monday, April 6, 2026
HomeWasanniCAF na binciken rashin ɗa’a a wasannin kwata-fainal na AFCON 2025 da...

CAF na binciken rashin ɗa’a a wasannin kwata-fainal na AFCON 2025 da suka shafi Nijeriya, Aljeriya, Kamaru da Maroko

Hukumar ƙwallon ƙafa ta Afirka (CAF) ta ƙaddamar da bincike kan zargin rashin ɗa’a daga wasu ’yan wasa da jami’ai a wasannin kwata-fainal na Kofin Ƙasashen Afirka AFCON 2025 tsakanin Kamaru da Maroko, da kuma Aljeriya da Nijeriya.

CAF ta ce ta ɗauki wannan mataki ne bayan samun rahotannin rikici da alkalai da kuma cikas da aka samu a wuraren bayan kammala wasanni, kamar yadda sanarwa a shafin yanar gizon CAF ta bayyana a ranar Litinin.

Sanarwar ta ce hukumar ta tattara rahotannin wasanni da faifan bidiyo da ke nuna yiwuwar halaye da ba su dace ba, tare da tura batun gaban Kwamitin Ladabtarwa domin ci gaba da bincike da ɗaukar mataki idan an samu laifi.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata