Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiCAN ta ce ba ta da masaniya kan sakin dalibai 100 a...

CAN ta ce ba ta da masaniya kan sakin dalibai 100 a jihar Neja

Kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) ta ce har yanzu ba ta samu takamaiman bayanin hukuma game da labarin sakin dalibai 100 daga cikin waɗanda aka sace a Papiri, Jihar Neja ba.

Shugaban kungiyar ta CAN na jihar, Bishop Bulus Yohanna, ya ce da labarin ya tabbata, da zai zama abin farin ciki, amma har yanzu ba su samu sanarwa daga hukumomi ba.

A ranar 21 ga Nuwamba 2025 ne ’yan bindiga suka kai farmaki makarantar St. Mary’s Private Catholic School, suka sace mutane 315, dalibai 303 da malamai 12.

Rahoton da gidan talabijin na Channels ta fitar ya nuna cewa gwamnati ta yi nasarar kubutar da dalibai 100, abin da tsohon Janar John Enenche ya yaba, yana mai cewa aikin ceton ba abu ne mai sauƙi ba.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata