Ministan sadarwa Dr. Bosun Tijani, ya ce shugaba Bola Ahmed Tinubu na aiki tukuru domin gina rayuwar matasa, al’umma da kuma makomar ƙasar baki ɗaya.
Dr. Tijani ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin buɗe gasar kwallon kwando ta matasa daya gudana a babban birnin jihar Ogun.
Ministan ya ce gasar, wadda ta zo daidai da bukukuwan ƙarshen shekara, an tsara ta ne domin samar da nishaɗi da haɗin kai, inda matasa za su haɗu, tare da kulla alaƙa mai ɗorewa ta hanyar aiki tare.
Ya ce, idan aka tallafa wa matasa a irin waɗannan wurare, suna bayyana basirarsu ba kawai a wasanni ba, har ma a matsayin shugabanni da masu ba da gudummawa ga al’umma.
Ya kara da cewa irin wadannan abubuwa sun yi daidai da manufar shugaba Tinubu na gina makomar matasan Nijeriya.
