Monday, April 6, 2026
HomeKetareCyril Ramaphosa ya amince da karin albashi ga 'yan siyasar Afirka ta...

Cyril Ramaphosa ya amince da karin albashi ga ‘yan siyasar Afirka ta Kudu

Shugaban Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa ya amince da karin albashi ga ‘yan siyasa da masu rike da madafun ikon kasar

 

Karin albashin nasu zai fara aiki ne a ranar 1 ga watan Afrilun 2026, kamar yadda fadar gwamnatin ƙasar ta bayyana.

 

DW Africa ta ruwaito cewa karkashin sabon tsarin albashin, mataimakin shugaban kasa zai rika karbar akalla Dala 177,000 a shekara, yayin da ministoci za su rika samun kusan Dala 151,000, sai kuma mataimakansu Dala 124,000.

 

Sai dai wannan mataki na gwamnatin Afirka ta Kudu ya bar baya da kura, inda wasu kungiyoyin ma’aikata da jam’iyyun siyasa ke sukar lamarin.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata