Ministan sufurin jiragen sama na Nijeriya Festus Keyamo, ya kare shirin gwamnatin tarayya na sake fasalta filin jirgin sama na Murtala Muhammed da ke Lagos da kudin na suka kai Naira biliyan 712, yana mai cewa hakan na da nufin yin gogayya da sauran filayen na duniya.
Yayin wata hira da tashar Channels Television a shirin Sunday Politics, Keyamo, wanda lauya ne mai matsayin SAN, ya bayyana cewa filin jirgin da aka gina sama da shekaru arba’in da suka wuce ya lalace matuka.
“Rufin tashar jirgin na yayyafa ruwa; wajen ya lalace kuma yana wari. Ana siyar da Indomie da wasu kayayyaki a ciki. Fankoki da ke tura kaya sun daina aiki saboda babu gyara,” in ji shi.
A makon da ya gabata, gwamnatin tarayya ta amince da kashe biliyan ₦712 don yin aikin, wanda hakan ya jawo cece-kuce daga jama’a da dama.
Daga cikin rarar tallafin man fetur za a yi wa filin jirgin saman Lagos gyaran Naira biliyan 712 – Festus Keyamo
Recent Comments
on Gwamnatin Tinubu za ta fara ba da rancen maras kuɗin ruwa ga manoma da masu ƙananan sana’o’i – GEEP
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Jaridar Daily Trust ta gano dalilai uku da suka sa Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC na kasa
on Peter Obi ya sake jaddada bukatar kafa tsarin wa’adin shekara 5 kacal ga shugaban ƙasa a Najeriya
on Cire tsoffin ‘yan sanda daga daga tsarin Contributory Pension Scheme ya fi karfina – IGP Egbetokun
on Gwamnatin Nijeriya ta ɗage buɗe shafin neman aiki na Immigration, Civil Defence da sauran hukumomi
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An karkatar da Naira Bilyan 71.2 daga cikin Bilyan 100 na bashin dalibai a Nijeriya – Hukumar ICPC
on Gwamna Abba Gida Gida ya zabi tsohon shugaban ma’aikatansa da wasu mutum 5 a matsayin kwamishinoni
on Nijeriya za ta zama jagorar kasuwar halal ta duniya mai jarin Dala bilyan Dubu 7 – Kashim Shettima
