Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiDalibai 50 cikin daliban jihar Neja da aka sace sun tsere daga...

Dalibai 50 cikin daliban jihar Neja da aka sace sun tsere daga hannun masu garkuwa da mutane – Kungiyar CAN

Dalibai 50 daga cikin waɗanda aka sace a makarantar St. Mary’s Secondary and Primary School da ke Papiri a ƙaramar hukumar Agwara ta jihar Neja sun tsere daga hannun ’yan bindiga kuma sun koma gidajensu lafiya.

A cewar shugaban Kungiyar Kiristoci Nijeriya reshen jihar Neja, Most Rev. Bulus Dauwa Yohanna, wanda shi ne mamallakin makarantar, waɗannan daliban sun kuɓuta ne a ranar Asabar kuma aka haɗa su da iyalansu, kamar yadda sanarwar sakatariyarsa ta bayyana a ranar Lahadi kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Rev. Yohanna ya ce makarantar na da ɗalibai 430 a aji na firamare, inda 377 suke na kwana. Ya ce yanzu haka, bayan waɗanda suka tsere, dalibai 236, 14 na sakandare da ma’aikata 12 na nan a hannun ’yan bindiga, yayin da hukumomin tsaro ke ƙoƙarin ceto su.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata