Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiDalilin da ya sa Buhari ya ba ni minista a gwamnatinsa -...

Dalilin da ya sa Buhari ya ba ni minista a gwamnatinsa – Lai Mohammed

Tsohon ministan yada labarai da al’adu na Nijeriya Lai Mohammed ya bayyana cewa shafe tsawon lokaci cikin rikon amana, biyayya da kuma hidima ne suka sanya tsohon shugaba Muhammadu Buhari ya ba shi mukamin minista a gwamnatinsa.

 

Lai Mohammed ya bayyana haka ne a cikin sabon littafin da ya kaddamar mai taken ‘Headlines and Soundbites: Media Moments that Defined an Administration’.

 

A cikin littafin da aka kaddamar a ranar 17 ga watan Disambar 2025 a Abuja, Lai Mohammed ya ce marigayi Muhammadu Buhari ya yi jinkiri kafin ya zabo mambobin kunshin gwamnatinsa.

 

Sai dai sakamakon yardar da tsohon shugaban ya masa, ya amince masa da kasancewa cikin kwamitin karbar mulki bayan samun nasara a zaben 2015.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata