Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiDangote ya yi barazanar neman hakkin Biliyan 100 a kotu bisa kalaman...

Dangote ya yi barazanar neman hakkin Biliyan 100 a kotu bisa kalaman batanci da wani dan kasuwa ya yi masa

Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Dangote, ya bai wa wani ɗan kasuwa mazaunin Kaduna, Kailani Mohammed, wa’adin kwana bakwai da ya janye kalaman da ya yi tare da neman afuwa a bayyane, ko kuma ya fuskanci ƙarar bata suna ta Naira biliyan 100 kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Hakan na cikin wata wasiƙa da lauyan Dangote, Ogwu Onoja (SAN), ya rubuta a ranar 20 ga Disamba, 2025, inda ya zargi Mohammed da yin kalaman ƙarya da rashin tushe kan tushen dukiyar Dangote da kuma zarginsa da “harkokin kasuwanci marasa tsafta” a shekarun 1980.

An ce kalaman sun fito ne a wata hira da TrustTV a ranar 17 ga Disamba, 2025, yayin da Mohammed ke tsokaci kan wani ƙorafi da aka kai wa ICPC game da tsohon shugaban NMDPRA, Alhaji Farouk Ahmed.

Lauyoyin Dangote sun ce kalaman sun ɓata masa suna matuƙa a cikin gida da ƙasashen waje, suna mai jaddada cewa Dangote sanannen ɗan kasuwa ne da ya gina dukiyarsa ta hanyar aiki tuƙuru da gaskiya, kuma duk wata magana akasin haka bata suna ce kai tsaye.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata