Tsohon mataimakin shugaban Nijeriya Atiku Abubakar ya nuna damuwa kan karancin fitowar masu kada kuri’a a zaben da aka gudanar ranar Asabar a Abuja.
Cikin wani sako da hadiminsa Paul Ibe ya wallafa a shafinsa na X, ya ce hakan na nuni da irin bazaranar da dimukuradiyya a Nijeriya ke fuskanta karkashin gwamnatin shugaba Tinubu.
Ya yi zargin cewa rashin fitowar masu zaɓe, na da alaka da yanayin tsoratarwa da kuma tauye ‘yancin yan adawa da ya ce ana yi a kasar, kamar yadda Channels TV ya wallafa.
