Monday, April 6, 2026
HomeKetareECOWAS ta amince John Mahama ya mata takarar shugabancin AU a 2027

ECOWAS ta amince John Mahama ya mata takarar shugabancin AU a 2027

Majalisar Ministocin ECOWAS ta amince da Shugaban Ghana, John Mahama, a matsayin ɗan takarar kungiyar da zai nemi kujerar Shugaban Kungiyar Tarayyar Afrika (AU) a shekarar 2027, lokacin da jagorancin zai koma yankin Yammacin Afrika.

An cimma wannan matsaya ne a taron ministocin karo na 95 da aka gudanar a Abuja, inda aka bayyana Ghana a matsayin muhimmiyar ƙasa a ECOWAS wadda ke ba da gudunmuwa ga martabar ƙungiyar a matakin duniya.

Jaridar Premium Times ta ambato Ministan Harkokin Wajen Ghana, Sam Ablakwa, ya bayyana cewa shugabannin kasashen ECOWAS za su tabbatar da wannan matsaya ranar Lahadi.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata