Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiEl-Rufa'i ba dan jam'iyyarmu ba ne - SDP

El-Rufa’i ba dan jam’iyyarmu ba ne – SDP

Jam’iyyar SDP ta bayyana cewa tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasir Ahmad El-Rufai, ba mambanta ba ne, tana zarginsa da keta doka da kokarin nuna kansa a matsayin wakilin jam’iyyar ba tare izini ba.

A wani taron manema labarai da ta gudanar a Kaduna ranar Juma’a, Sakataren SDP na shiyyar Arewa maso Yamma, Alhaji Idris Inuwa, ya bayyana cewa “El-Rufai ba mamban jam’iyyar SDP ba ne kuma bai taɓa zama ba.”

Ya kuma gargadi jama’a da masu ruwa da tsaki da su yi watsi da duk wata magana da yayi da sunan jam’iyyar.

Inuwa ya ce: “Ya zama dole a fayyace – Malam El-Rufai ba shi da wani izini ko wakilci daga SDP a kowane mataki. Abinda yake yi wani babban laifi ne na keta doka da kuma neman bata wa jam’iyyar suna.”

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata