Wednesday, April 8, 2026
HomeLabaraiFadar mai alfarma sarkin musulmi ta ayyana ranar Litinin a matsayin ranar...

Fadar mai alfarma sarkin musulmi ta ayyana ranar Litinin a matsayin ranar 1 ga watan Rajab 1447AH

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da kwamitin ba da shawara kan harkokin addini, tare da haɗin gwiwar kwamitin duban wata suka fitar a ranar Asabar, 20 ga Disamba, 2025.

Sanarwar ta bayyana cewa ba a samu rahoton ganin jinjirin watan Rajab ba daga ko ina a fadin Nijeriya a daren Asabar wanda ya yi daidai da 29 ga watan Jumada Sani, don haka watan ya cika kwana 30.

Sakamakon haka, Mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar, ya amince da rahoton tare da ayyana Litinin a matsayin 1 ga watan Rajab.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata