Tsohon Gwamnan Jihar Ekiti, Dr Kayode Fayemi, ya musanta rahotannin da ke cewa ya yi wata ganawa da tsohon Gwamnan Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, a gidansa da ke Abuja.
A wata sanarwa da shugaban ofishin yaɗa labaransa, Ahmad Sajoh, ya fitar a ranar Alhamis, Fayemi ya bayyana rahoton a matsayin ƙarya, yana mai buƙatar jama’a su yi watsi da shi.
Rahoton ya bazu ne a kafafen sada zumunta, musamman X (Twitter), tare da wani tsohon bidiyo da ke nuna Fayemi yana gaisawa da Kwankwaso.
Sai dai a sanarwar da jaridar Punch ta ambato ya ce ya haɗu da Kwankwaso sau ɗaya ne kacal cikin shekara guda, kuma hakan ya faru ne a taron ƙaddamar da littafi na tsohon Babban Lauyan Ƙasa, Mohammed Bello Adoke, SAN.
Sanarwar ta ƙara da cewa Fayemi bai taɓa yin wata ganawar siyasa ta sirri da Kwankwaso ba, kuma ba ya shirin yin hakan.
