Hadimin shugaban Nijeriya, Daniel Bwala, ya ce kusan kashi 70 cikin 100 na mutanen da ke aiki tare da Tinubu sun taba adawa da shi a baya.
Bwala ya bayyana haka ne a Arise TV yayin martani kan sukar jerin sunayen jakadu da cewa wasu sun taba yi wa Tinubu ihu a siyasance.
Bwala ya ce Tinubu ya sha gaya masa cewa mahaifiyarsa ta koya masa rungumar kowa ko da masu adawa ne, kuma fadar shugaban kasa ta yi shiru kan jerin jakadu ne don kada ta tsoma baki a aikin Majalisa.
Hakazalika ya kara da cewa tarihin Tinubu ya nuna cewa yawancin mutanen da ke kusa da shi a yau sun taba kalubalantar sa a siyasa, amma ya yanke shawarar yin aiki da su saboda salon shugabancinsa.
