Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiGanduje na shirin kafa sabuwar kungiyar sa-kai mai kama da Hisbah

Ganduje na shirin kafa sabuwar kungiyar sa-kai mai kama da Hisbah

Tsohon Shugaban jam’iyar APC a Nijeriya Dr Abdullahi Umar Ganduje ya sanar da shirin kafa wata sabuwar ƙungiya mai kama da Hisbah, karkashin Cibiyar Ganduje Foundation domin karɓar ma’aikatan Hisbah 12,000 da gwamnatin jihar ta sallama daga aiki.

Wannan na zuwa ne bayan Ganduje ya karɓi rahoton kwamitin tantance waɗanda aka sallama daga aiki.

Jaridar Daily Trust ta rawaito Ganduje na bayyana sallamar a matsayin rashin adalci kuma abin da ya tilasta nemo musu mafita.

Da yake jawabi ga kwamitin da Gandujen ya kafa kan batun, ya ce sabuwar rundunar da za a yi za ta kasance mai zaman kanta da za ta ba da dama ga duk wanda ya ke son shiga ciki har da waɗanda ba su kasance cikin mutum 12,000 ɗin da aka sallama.

Ya bayyana cewa tsohon Kwamandan Hisbah, Sheikh Muhammad Harun Ibn Sina shi ne zai jagoranci aikin kafa wannan runduna, wacce za ta yi aiki irin na Hisbah, ciki har da wayar da kai, taimakon gaggawa, yi wa jama’a nasiha da kuma taimako a lokutan bukata.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata