Wednesday, April 8, 2026
HomeKetareGasar cin kofin kasashen nahiyar Afirka AFCON za ta koma duk bayan...

Gasar cin kofin kasashen nahiyar Afirka AFCON za ta koma duk bayan shekaru 4 – CAF

Hukumar kwallon kafa ta nahiyar Afrika CAF, ta sanar da cewa gasar cin kofin kasashen Afrika AFCON, za ta koma duk bayan shekara huɗu bayan kammala gasar da aka tsara a 2028.

Shugaban na CAF, Patrice Motsepe, ne ya bayyana hakan a ranar Asabar yayin ganawa da manema labarai a Rabat, da ke Maroko, inda ya ce sauyin yana cikin gyaran tsarin wasannin ƙwallon ƙafa a nahiyar domin ya dace da jadawalin wasannin duniya.

Motsepe ya bayyana cewa duk da AFCON na taimaka wa ƙungiyoyin ƙasashe ta fuskar kuɗaɗe, CAF ta yanke shawarar ƙaddamar da gasar African Nations League wadda za a rika yi kowace shekara, makamanciyar UEFA Nations League.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata