Monday, April 6, 2026
HomeSiyasaGaskiyar dalilan murabus din Badaru

Gaskiyar dalilan murabus din Badaru

Bayan murabus dinsa kwatsam daga kujerar Ministan Tsaro, wasu bayanai sun bayyana kan ainihin dalilin da ya sa Abubakar Badaru ya sauka daga mukaminsa bayan shekara biyu kacal a ofis.

A ranar Litinin, Badaru ya sanar da murabus ɗinsa yana mai cewa dalilan lafiya ne suka tilasta masa daukar matakin.

Jaridar Punch ta ruwaito yaddda Shugaba Bola Tinubu ya rantsar da sabon Ministan Tsaro, tsohon CDS, Janar Christopher Musa (Rtd.), domin ya maye gurbinsa.

Mai ba shugaban kasa shawara kan bayanai da dabarun yada labarai, Bayo Onanuga, ya ce murabus ɗin na da alaƙa da “ƙarin matsalolin lafiya.”

Amma binciken da Saturday PUNCH ta gudanar ya gano cewa rikici mai tsawo tsakanin Badaru da karamin Ministan Tsaro, Bello Matawalle, shi ne ainihin dalilin da ya tilasta masa murabus — ba matsalar lafiya kawai ba.

Badaru dai ya hau kujerar minista ne a Agusta 21, 2023, bayan kammala wa’adin gwamnan Jigawa.

Inda aka nada shi bisa kwarewar mulki da tasirinsa a Arewa maso Yamma, yankin da ke fama da hare-haren ‘yan bindiga da ta’addanci.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata