Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiGwamna Uba Sani ya zabtare kudin rajistar manyan makarantun jihar Kaduna

Gwamna Uba Sani ya zabtare kudin rajistar manyan makarantun jihar Kaduna

 

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya sanar da rage kudin rajistar shiga manyan makarantun jihar, a wani mataki na rage tsadar rayuwar da ke addabar jama’a ciki har da Kaduna. Sanarwar da DCL Hausa ta samu a kan wannan batu ta nuna cewa yanzu kudaden rajistar makaratun jihar sun koma kamar haka:

Jami’ar Jihar Kaduna 

– Kudin makarantar sun koma 105,000 a maimakon N150,000
Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Nuhu Bamalli 
– Kudin makarantar sun koma N50,000 a maimakon N100,000
Kwalejin Kiwon Lafiya ta Shehu Idris Makarfi
-HND: N70,000 a maimakon N100,000
-ND: 52,000 a maimakon N75,000
Wannan na zuwa ne a kwanaki kalilan bayan da wasu mata a jihar ta Kaduna suka yi zanga-zangar tsadar rayuwa.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata