Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiGwamnan Adamawa Ahmadu Fintiri ya ce taron PDP babu gudu babu ja...

Gwamnan Adamawa Ahmadu Fintiri ya ce taron PDP babu gudu babu ja da baya

Gwamnan jihar Adamawa kuma shugaban kwamitin shirya babban taron jam’iyyar PDP, Ahmadu Fintiri, ya tabbatar da cewa jam’iyyar ta yanke hukuncin gudanar da babban taron jam’iyya a garin Ibadan.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa Gwamna Fintiri ya bayyana hakan ne yayin zantawa da manema labarai, bayan wani muhimmin taron jiga-jigan jam’iyyar da aka gudanar a Abuja.

Taron ya samu halartar Gwamnan Oyo, Seyi Makinde, Amb. Umar Damagum, Bukola Saraki, kakakin jam’iyyar, Debo Ologunagba, da sauran manyan jiga-jigai a cikinta.

Fintiri ya ce taron ya tattauna muhimman batutuwa da dama, yana mai jaddada cewa zasu tafi Ibadan domin babban taronsu, kuma wannan kudiri ba zai canza ba.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata