Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiGwamnan Kebbi ya soki rundunar sojin Nijeriya kan yadda take yakar rashin...

Gwamnan Kebbi ya soki rundunar sojin Nijeriya kan yadda take yakar rashin tsaro

Gwamnan jihar Kebbi Nasir Idris ya nuna rashin gamsuwa da tsarin da rundunar soji ke amfani da shi wajen yakar rashin tsaro yana mai kira da a sauya dabarar aiki.

Gwamman ya bayyana haka ne a Litinin din nan lokacin da ya karɓi bakuncin ‘yan Majalisar wakilai karkashin jagorancin kakakin Majalisar Tajudeen Abbas a gidan gwamnati da ke Birnin Kebbi.

Jaridar Daily Trust ta rawaito gwamnan na sake jaddada bukatar yin bincike kan janye jami’an tsaro daga makarantar ta ‘yan mata ta Maga mintuna kaɗan kafin ’yan bindiga su sace ’yan mata 25.

A cewar gwamnan abin mamaki ne yadda ‘yan bindiga fiye da 500 ke yawo a babura a manyan hanyoyi ba tare da an dakatar da su ba, duk da cewa gwamnati na ba da tallafi, kayan aiki, da motoci ga jami’an tsaro.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata