Gwamnan Legas Babajide Sanwo-Olu ya shirya gabatar da Naira tiriliyan 4.2 a matsayin kasafin kudin jihar na shekarar 2026.
Jaridar Punch ta ruwaito yadda majalisar dokokin jihar ta tabbatar da karbar bukatar gwamnan a cikin wata wasika da ya aike mata, yana mai neman ta tsayar masa da rana don zuwa ya gabatar.
Sai dai har zuwa lokacin wallafa wannan labari dai, majalisar ba ta tsayar da ranar da za ta gayyaci gwamnan don ya gabatar da kasafin ba.
