Wata sabuwa ta kunno kai a jihar Neja bayan da Gwamna Mohammed Umaru Bago ya bayar da umarnin rufe gidan rediyo na Badeggi FM da ke Minna, babban birnin jihar, lamarin da ya janyo cece-kuce da suka daga kungiyoyin ‘yan jarida da masu kare hakkin ‘yan kasa ciki har da Amnesty International.
A cewar sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Bologi Ibrahim ya fitar, gwamna Bago ya bayar da umarnin a rufe gidan rediyon tare da kwace lasisin aikinsa da kuma binciko bayanan mamallakinsa, a yayin wani taron jam’iyyar APC da aka gudanar a gidan gwamnatin jihar.
Sanarwar ta kara da cewa gwamnan ya zargi gidan rediyon da tayar da fitina da tunzura jama’a kan gwamnati, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.
Shugaban gidan radiyon na Badeggi FM Abubakar Shuaib, ya mayar da martani ga wannan mataki, yana mai cewa ya kamata gwamnan ya bi hanyar doka wajen gabatar da korafe-korafensa, maimakon tura jami’an tsaro su tsoratar da ma’aikatan rediyon ko mamallakinsa.
Gwamnan Neja na shan suka bayan ba da umurnin rufe wani gidan rediyo a jihar
Recent Comments
on Gwamnatin Tinubu za ta fara ba da rancen maras kuɗin ruwa ga manoma da masu ƙananan sana’o’i – GEEP
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Jaridar Daily Trust ta gano dalilai uku da suka sa Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC na kasa
on Peter Obi ya sake jaddada bukatar kafa tsarin wa’adin shekara 5 kacal ga shugaban ƙasa a Najeriya
on Cire tsoffin ‘yan sanda daga daga tsarin Contributory Pension Scheme ya fi karfina – IGP Egbetokun
on Gwamnatin Nijeriya ta ɗage buɗe shafin neman aiki na Immigration, Civil Defence da sauran hukumomi
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An karkatar da Naira Bilyan 71.2 daga cikin Bilyan 100 na bashin dalibai a Nijeriya – Hukumar ICPC
on Gwamna Abba Gida Gida ya zabi tsohon shugaban ma’aikatansa da wasu mutum 5 a matsayin kwamishinoni
on Nijeriya za ta zama jagorar kasuwar halal ta duniya mai jarin Dala bilyan Dubu 7 – Kashim Shettima
