Monday, April 6, 2026
HomeSiyasaGwamnan Osun Adeleke ya fice daga jam’iyyar PDP

Gwamnan Osun Adeleke ya fice daga jam’iyyar PDP

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya sanar da ficewarsa daga jam‘iyyar PDP, yana mai bayyana rigingimun cikin gida a matsayin dalilin daukar matakin.

 

Cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, gwamna Adeleke ya tabbatar da cewa ya mika takardar ficewar ga masu ruwa da tsaki na jam’iyyar a jihar tasa.

 

Jaridar Punch ta ruwaito cewa ficewar ta zo ne sa’o’i kadan bayan da aka yi hasashen cewa gwamnan ba zai sake neman tsayawa takara a jam’iyyar ba, har sai an shawo kan matsalolin da jam’iyyar ke fuskanta a tsakar gidanta na siyasa.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata