Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiGwamnan Zamfara zai yi karin albashi ga Malaman Addini

Gwamnan Zamfara zai yi karin albashi ga Malaman Addini

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya sanar da shirin ƙara albashi ga limaman Juma’a 11,300 da malaman addinin Musulunci a faɗin jihar, inda sabon tsarin zai fara aiki daga Janairu 2026.

Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin da ya ke ganawa da Malaman addini.

Ya jaddada kudirin gwamnatinsa na inganta walwala da yanayin malamai da limamai a jihar.

A cewarsa, gwamnatin jihar na kashe Naira miliyan 81.8 a kowane wata wajen biyan alawus-alawus ga limamai, malamai da masu tsaftace masallatai.

Ya ce shirin ya biyo bayan shawarar kwamitin da gwamnan ya nada inda ya ba da shawarar a kara albashinsu.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata