Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiGwamnati ta bukaci ‘yan Nijeriya da su kwantar da hankalinsu kan barazanar...

Gwamnati ta bukaci ‘yan Nijeriya da su kwantar da hankalinsu kan barazanar Trump

Gwamnatin Nijeriya ta bukaci ’yan kasar su kwantar da hankalinsu dangane da sabanin diflomasiyya da ke tsakaninta da Amurka.

Ministan yada labarai Alhaji Mohammed Idris ne ya yi wannan kira yayin da ya kai ziyarar ban girma ga gwamnan jihar Jigawa, Malam Umar Namadi a ranar Litinin.

A cewar sanarwar da Malam Rabiu Ibrahim, mataimakin minista na musamman kan yada labarai ya fitar a Abuja, Idris ya je Jigawa ne domin halartar taron matasan Arewa maso Yamma na 2025 da kuma gabatar da nasarorin da shugaba Tinubu ya cimma cikin shekaru biyu da suka gabata.

Ministan ya ce shugaba Tinubu na da cikakkiyar kwarewa da karfin guiwa wajen kare martabar Nijeriya da gyara duk wata matsala ta dangantaka da kasashe abokan hulɗa.

A cewarsa, ’yan Nijeriya kada su firgita, su kwantar da hankali, Tinubu zai iya warware lamarin cikin lumana kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata