Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiGwamnatin Amurka na aiki da ta Nijeriya domin kawo karshen musguna ma...

Gwamnatin Amurka na aiki da ta Nijeriya domin kawo karshen musguna ma Kiristoci da ‘yan ta’adda ke yi a kasar – Sakataren tsaron Amurka

Gwamnatin Amurka ta ce gwamnatin shugaba Donald Trump na aiki tare da gwamnatin Nijeriya domin kawo ƙarshen abin da ta kira zaluntar Kiristoci da ’yan tada kayar baya ke yi a kasar, kamar yadda sakataren tsaron Amurka Pete Hegseth ya bayyana.

Hegseth ya bayyana haka ne a shafinsa na X da Facebook bayan ganawarsa da mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu, da tawagarsa a Amurka.

A cewar sakataren, sun tattauna kan tashin hankaulan da ke addabar Kiristoci a Nijeriya, inda ya ce gwamnatin Trump na kokari sosai don dakile hare-haren da ake danganta wa ’da ‘yan tada kayar baya.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa Ribadu ya jagoranci tawaga mai ƙarfi zuwa Amurka domin tattaunawa kan zargin zaluntar Kiristoci a Nijeriya, inda kuma kafin haka shugaba Trump ya sanya Nijeriya cikin jerin ƙasashen da ake kallon suna da matsalar tauye ’yancin addini.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata