Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiGwamnatin Bauchi ta dakatar da wasu manyan ma'aikatan gwamnati a jihar

Gwamnatin Bauchi ta dakatar da wasu manyan ma’aikatan gwamnati a jihar

Hukumar Kula da Ma’aikatan Gwamnati ta Jihar Bauchi ta dauki matakin ladabtar da wasu manyan ma’aikata huɗu saboda gagarumin cin amanar aiki a yayin gudanar da ayyukansu.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na hukumar, Mista Saleh Umar, ya fitar wa manema labarai a Bauchi ranar Juma’a.

Umar ya ce wannan mataki da aka dauka yayin zaman majalisar hukumar, na daga cikin ƙoƙarin da ake yi domin tsaftace harkokin aikin gwamnati a jihar.

Ya bayyana sunayen ma’aikatan da abin ya shafa kamar haka: Garba Hussaini, Darakta (Ilimi) kuma tsohon Provost; Haruna Umar, Mataimakin Darakta (Gudanarwa da Harkokin Ma’aikata); Umar Yusuf, Babban Jami’in Gudanarwa – Bursar; da Mohammed Usman, – Cashier; dukkaninsu na aiki ne a Kwalejin Fasahar Kimiyyar Lafiya ta Bill and Melinda Gates da ke Karamar Hukumar Ningi.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata